Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci, saboda rikicin da ke ƙara tsananta a yankin gabas ta tsakiya kamar yadda wani rahoto ya bayyana.
Rahoton wanda jaridar Bloomberg ta wallafa, ya ce an ɗauki matakin ne saboda yiwuwar samun ƙarancin makamashi sakamakon yaƙin da ke faruwa a yankin.
China na daga cikin manyan ƙasashen da ke shigar da danyen mai kasarta daga waje, kuma tana cikin ƙasashen Asiya da ke dogaro da mashigin ruwa na Hormuz wajen jigilar makamashi.



