Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa.
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban Tinubu Bayo Onanuga ya fitar, Tinubu ya ce tasirin Obasanjo a Nijeriya Afirka da ma duniya baki ɗaya yana da girma sosai.
Shugaban ya jaddada cewa Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa ƙasa hidima, inda ya taba zama shugaban mulkin soja daga shekarar 1976 zuwa 1979, kafin ya miƙa mulki ga gwamnatin farar hula a 1979.
Haka kuma ya sake zama shugaban ƙasa na farar hula a jamhuriya ta huɗu daga 1999 zuwa 2007.



