DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

-

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban Tinubu Bayo Onanuga ya fitar, Tinubu ya ce tasirin Obasanjo a Nijeriya Afirka da ma duniya baki ɗaya yana da girma sosai.

Google search engine

Shugaban ya jaddada cewa Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa ƙasa hidima, inda ya taba zama shugaban mulkin soja daga shekarar 1976 zuwa 1979, kafin ya miƙa mulki ga gwamnatin farar hula a 1979.

Haka kuma ya sake zama shugaban ƙasa na farar hula a jamhuriya ta huɗu daga 1999 zuwa 2007.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Jami’ar gwamnatin tarayya da ke Dutse a jihar Jigawa ta kori dalibai 20 tare da dakatar da wasu 15 bisa zarginsu da satar jarrabawa

Jami'ar tarayya da ke jihar Jigawa ta kori dalibai 20 tare da dakatar da wasu 15 daga karatu bisa samunsu da laifin satar jarabawa. Rahotanni sun...

Mafi Shahara