DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin Tinubu

-

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba su a ƙasar.

Ministan harkokin cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo, ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis a Abuja yayin taron nazarin ayyukan ma’aikatar cikin gida na shekarar 2026.

Google search engine

Ministan ya ce gwamnati yanzu tana da cikakkun bayanan dukkan mutanen da suka shiga Nijeriya cikin shekaru goma da suka gabata, wanda hakan ke ba jami’an gwamnati damar gano waɗanda suka karya dokar zaman ƙasar.

Ya ce an samu wannan cigaba ne bayan kafa cibiyoyin kula da ayyuka na zamani a hukumar kula da shige da fice ta Nijeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara