DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ana hasashen ministocin Tinubu 4 za su ajiye aiki don neman wasu mukamai a 2027 – Jaridar Punch

-

Rahotanni na nuna cewa akalla ministoci hudu a gwamnatin Bola Ahmed Tinubu na shirin ajiye mukamansu domin neman wasu mukaman siyasa a jihohinsu gabanin babban zaben 2027.

Jaridar PUNCH ta ruwaito cewa daga cikin ministocin da ake zargin suna da wannan buri akwai ministan wutar lantarki Adebayo Adelabu, ministan lafiya Muhammad Ali Pate, ministan harkokin waje Yusuf Maitama Tuggar, da kuma karamin ministan kwadago Nkeiruka Onyejeocha.

Google search engine

Bincike ya nuna cewa wadannan ministoci na duba yiwuwar tsayawa takarar gwamna ko kuma wasu mukaman siyasa a jihohinsu, musamman a jihohin da gwamnoni za su kammala wa’adin mulkinsu na biyu a shekarar 2027.

Dokar zabe ta tanadi cewa duk wani mai rike da mukamin gwamnati da aka nada dole ne ya ajiye mukaminsa kafin ya shiga zaben fidda gwani a kowace jam’iyya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara