DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ba haka ake zawarcin shiga jam’iyya ba, Gwamna Abba ya yi wa Ganduje martani

-

 Ba haka ake zawarcin shiga jam’iyya ba, Gwamna Abba ya yi wa Ganduje martani

Google search engine

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf  ya ce ba shi da niyyar ficewa daga jam’iyyar sa ta (NNPP) da ya ci zabe a karkashinta. 

Gwamna Abba ya bayyana hakan ne kwana daya bayan da shugaban jam’iyyar APC Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya bashi goron gayyatar komawa jam’iyyar APC.

Gwamna Abba Kabir, wanda kotun koli ta tabbatar da shi a matsayin Gwamnan jihar Kano a ranar Juma’a 12 ga watan Janairu shi ne kadai gwamna a jam’iyyar NNPP a Nijeriya.

A yayin taron masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC da ya gudana a  Kano, Ganduje ya yi kira ga Gwamna Abba Kabir tare da mambobinsa da magoya bayansa na jam’iyyar NNPP da su sauya sheka zuwa jam’iyyar APC mai mulki a matakin kasa domin tabbatar da ci gaban siyasar jihar Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kamfanin NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar man birnin Port Harcourt

Kamfanin man fetur na Nijeriya NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar mai ta Fatakwal ga yan kasuwa A Yayin wani taro da kamfanin ya gabatar...

Tattalin arzikin Najeriya zai bunkasa daga 2025 zuwa 2026 – IMF

Asusun Lamuni na Duniya (IMF) ya sabunta hasashensa kan ci gaban tattalin arzikin Najeriya, inda ya ce zai kai kashi 3.4 cikin 100 a shekarar...

Mafi Shahara