DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kungiyar ECOWAS za ta yi zama kan harajin da kasashen Nijar, Mali da Burkina Faso suka ƙaƙaba wa ƙasashen kungiyar

-

Kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika ECOWAS za ta gudanar da taro a cikin watan Afrilun da muke domin tattaunawa kan harajin kashi 0.5 cikin 100 na shigo da kaya da kasashen yankin Sahel suka ƙaƙaba wa ƙasashen kungiyar ECOWAS a baya-bayan.
Shugaban sashen yaɗa labarai na Hukumar ECOWAS Joel Ahofodji, ya tabbatar da cewa majalisar kungiyar za ta yi taro a ranar 22 ga Afrilu don tattaunawa kan lamarin da sauran batutuwan da suka shafi kasashen, a cewar jaridar Dailytrust.
Da aka tambaye shi ko ECOWAS za ta dauki wani mataki na ramuwa dangane da harajin kashi 0.5 da AES suka sanya, Joel Ahofodji ya bayyana cewa, kungiyar za ta tattauna kan matakin da zata dauka a lokacin taron.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Atiku Abubakar ya caccaki hukumar EFCC kan tsare tsohon dan majalisa Gudaji Kazaure

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya soki hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta EFCC, kan tsare tsohon dan...

Gwamnatocin Pakistan da Indiya sun amince da tsagaita wuta a Asabar dinnan

Ministan harkokin wajen Pakistan Ishaq Dar ya sanar a shafinsa na X cewa, kasashen sun amince da Shirin tsagaita wuta cikin gaggawa. Shugaba Trump ya sanar...

Mafi Shahara