DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotu ta umarci gwamnatin Rivers da ta biya al’ummar da aka yi wa rusau ba bisa ka’ida ba diyyar sama da Naira biliyan 1

-

Jihar Rivers 

Wata babbar kotu a jihar Rivers ta bawa gwamnatin jihar umarnin cewa ta biya diyyar Naira biliyan 1 da miliyan 100 ga mutanen da aka rushewa kadarorinsu ba bisa ka’ida ba a Mile One da Mile Two da ke karamar hukumar Fatakwal.

Da yake yanke hukunci a Larabar nan mai shari’a Sika Aprioku, yace gwamnatin ba ta sanar da al’ummar da abin ya shafa ba kafin ta yi rusau din, inda ya ce, kotun ta samu gwamnati da laifin kwace musu filayensu da karfi.

Google search engine

Tun a shekarar 2022 ne dai, mazauna jihar da abin ya shafa, suka shigar gwamnatin kara gaban kotu bisa zargin tauye hakkokinsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Manyan Jami’an soji za su fuskanci ritayar dole bayan sauye-sauye a fannin tsaron Nijeriya

Rahotanni sun tabbatar da cewa akwai manyan jami'an sojin Nijeriya  masu mukamin Janar akalla 60 da za su fuskanci ritayar dole, biyo bayan sauye-sauyen da...

Rashin gogewar siyasa ta sa ban tsayar da El-Rufa’i don ya gaje ni ba – Obasanjo

Tsohon shugaban Nijeriya Olusegun Obasanjo ya bayyana cewa ya ki tsayar da tsohon gwamnan jihar Kaduna Malam Nasiru Elrufa'i don ya gaje a shekarar 2007...

Mafi Shahara