DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ministan Abuja Nyesom Wike ya ba da umarnin rufe asibitocin da aka yisu ba bisa ka’ida ba

-

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya ba da umurnin rufe duk wani asibitin da ba a yi wa rajista ba da kuma ma’aikatan jinya da ke aiki a babban birnin tarayya Abuja.

Babban mataimaki na musamman ga ministan kan harkokin yada labarai Olayinka ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a Abuja ranar Asabar.

Google search engine

Olayinka ya bayyana cewa ministan ya bayar da umarnin ne a lokacin da yake magana kan mutuwar wata mata mai juna biyu a wani asibiti mai zaman kansa da ke Durumi, Abuja, bayan tiyatar da aka yi mata.

A cewarsa, ministan ya yi gargadin cewa duk wanda aka samu yana gudanar da aikin ta haramtacciyar hanya ko kuma yana aiki a wani asibiti da bashi da rajista to a kama shi kuma a hukunta shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara