Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiECOWAS ta yi kira ga Nijar, Mali da Burkina Faso su sake...

ECOWAS ta yi kira ga Nijar, Mali da Burkina Faso su sake shiga kungiyar

Majalisar kungiyar kasashen yammacin Africa wato ECOWAS ta yi kira ga kasashen Mali, Burkina Faso da Nijar da su sake nazari kan matakin ficewar cikin kungiyar.

A karshen wani taro na kwanaki biyar da majalisar ta yi a birnin Banjul na kasar Gambia, shugaban kwamitin hadin gwiwa Sanata Edwin Melvin Snowe Jr., ya jaddada muhimmancin hadin kai tsakanin kasashen da ke yankin.

Sanata Edwin ya bayyana ficewar kasashen uku a matsayin wani abu da ya yi wa kasashen zafi, yana mai cewa kungiyar ta kasance a haɗe tsawon shekaru hamsin da suka gabata sai yanzu da kasashen suka fice.

Kasashe uku na yankin Sahel wadanda sojojin da suka yi juyin mulki ke jagoranta a yanzu, sun sanar da ficewa daga kungiyar ECOWAS ne a ranar 28 ga watan Junairu, 2024, kuma ficewar ta fara aiki ne a watan Janairun 2025.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

1 COMMENT

  1. Baikamata sudawoba domin ECOWAS batada manifesto illa biyawa turawa bukatunsu,,
    Kuma kozasu komai sai bayan BOLA TINUBU yabar shugabanchin ECOWAS,
    Sanan a zauna a Yi sabon tsari domin samun chigaban Africa ta yamma da Kuma hadewar Africa guri daya,

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata