DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tsohon gwamnan jihar Kaduna Malam Nasir El Rufa’i ya fice daga jam’iyyar APC ya kuma SDP

-

Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru El-Rufai ya fice daga jam’iyyar APC mai mulki a Nijeriya ya koma jam’iyyar SDP.

Google search engine

Tsohon gwamnan ya bayyana ficewar sa a shafinsa na Facebook yana mai cewa “daga yau 10 ga Maris na shekarar 2025 na fice daga jam’iyyar APC”.

Nasir El-Rufai ya bayyana cewa a shekara biyun da jam’iyyar APC ta yi babu wani abin a zo a gani da ta aiwatar ga ‘yan kasa.

Tsohon gwamnan ya jaddada cewa zamansa na shekaru takwas a matsayin gwamnan jihar Kaduna ya samar da ci gaba a fannin ilimi da kiwon lafiya da ababen more rayuwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dangote ya janye korafin zarge-zargen cin hanci da ya shigar a hukumar ICPC kan Farouk Ahmed

Dangote ya janye korafin zarge-zargen cin hanci da ya shigar a hukumar ICPC kan Farouk Ahmed, tsohon shugaban hukumar NMMPRA Jaridar Daily Trust ta ce attajirin...

Nijeriya na bin kasashen Nijar, Togo da Benin tulin bashin kudin lantarkin da ya kai N25bn – NERC

Hukumar kula da lantarki ta Nijeriya NERC ta ce, kasar na bin kasashen Togo, Nijar da Benin bashin dala $17.8m — kimanin N25bn na lantarkin...

Mafi Shahara