DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Da yiwuwar a samu ambaliyar ruwa a jihohi 12 na Nijeriya – NEMA

-

Hukumar ba da agajin gaggawa a Nijeriya NEMA, ta yi kira ga jihohin kasar da su zamo cikin shiri domin tunkarar ambaliyar ruwa da ke iya afkuwa a daminar bana, 2025.

Hukumar ta ce za ta aika tawaga kowace Jiha domin tattataunawa da al’ummar da ake sa ran faruwar ambaliyar domin gargadi da kuma zama cikin shirin ko-ta-kwana.

Darakta Janar ta NEMA, Malama Zubaida Umar ce ta bayyana hakan a wani taron masu ruwa da tsaki da ya gudana a Abuja.

Sai dai, hukumar ta NEMA ba ta ambaci sunayen jihohi da kananan hukumomin da ake sa ran ambaliyar ruwan za ta afku ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Sabon Paparoma ya gayyaci Shugaba Tinubu zuwa Rome, Italy

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya amsa goron gayyatar da sabon Paparoma Pope Leo XIV ys yi masa zuwa birnin Rome na kasar Italy. Daga cikin tawagar...

‘Yan sanda a jihar Nasarawa sun kama wata mata da makamai za ta kai su Katsina

Rundunar ‘yan sandan jihar Nasarawa ta bayyana cewa jami’anta, sun kama wata mata da ake zargi da safarar makamai ga barayin daji. Mai magana da...

Mafi Shahara