DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Flying Eagles ta sha kashi a hannun Afrika ta Kudu da ci 1-0 a wasan dab da na karshe na AFCON U-20

-

Kasar Afirka ta Kudu ta doke ‘yan wasan Flying Eagles na Nijeriya da ci 1-0 a wasan dab da na karshe na gasar cin kofin nahiyar Afrika na ‘yan kasa da shekaru 20.

An buga wasan ne a filin wasa na Suez Canal ranar Alhamis, don samun tikitin zuwa wasan karshe na gasar AFCON ta ‘yan kasa da shekaru 20 a kasar Masar.

Google search engine

Nasarar ta ba Afirka ta Kudu damar kaiwa wasan karshe na AFCON U-20 karo na biyu a tarihin ta, karon farko tun 1997, lokacin da suka kare a matsayin na biyu.

Ga Nijeriya kuwa, wannan shi ne karo na uku a jere da ta sha kaye a matakin wasan kusa da na karshe, bayan da Gambiya ta doke ta a shekarar 2023 da Mali a 2019.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara