DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Saura kiris a dakatar da ni saboda na bayyana albashin Sanatoci a 2018 – Shehu Sani

-

Shehu Sani

Tsohon sanata mai wakiltar Kaduna ta tsakiya, Shehu Sani, ya bayyana cewa da kyar ya tsallake rijiya, bayan da majalisar dattawa ta yi yunkurin dakatar da shi a shekarar 2018 saboda ya bayyana albashi da alawus-alawus na ‘yan majalisar Dattawa.

A cewar Shehu Sani, ba don shugaban majalisar dattawa na lokacin Bukola Saraki da mataimakinsa Ike Ekweremadu sun sanya baki ba, shima da an dakatar da shi na tsawon watanni shida.

Google search engine

Ya bayyana hakan ne a wani sako da ya wallafa a shafinsa na X bayan dakatar da Sanatar Kogi ta tsakiya, Natasha Akpoti-Uduaghan.

Jaridar Punch ta rawaito Shehu Sani na cewa, muddin mutum yana cikin majalisa kuma ya fallasa wani abu to babu wani Sanata da zai goyi da bayansa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar wakilan Nijeriya ta amince wa Tinubu ya ciyo bashin dala biliyan 2.35

Majalisar wakilai ta Nijeriya ta amince da bukatar shugaban Tinubu na neman bashin dala biliyan 2.347 daga ƙasashen waje domin cike gibin kasafin kuɗin 2025...

Sojojin Nijeriya za su murƙushe ‘yan ta’addan Lakurawa — Babban hafsan sojin kasa Janar Waidi Shaibu

Babban hafsan sojin kasa, Manjo Janar Waidi Shaibu, ya sha alwashin murƙushe sabuwar ƙungiyar ‘yan ta’addan Lakurawa wadda ke addabar wasu sassan arewacin Nijeriya. Janar Shaibu,...

Mafi Shahara