Sunday, April 5, 2026
HomeBabban LabarinmuDangote ya sanar da sake rage farashin litar man fetur dinsa da N15

Dangote ya sanar da sake rage farashin litar man fetur dinsa da N15

Matatar mai ta Dangote ta sanar da rage farashin man fetur a sassa daban daban na Nijeriya, inda a yanzu haka farashin ya koma tsakanin N875 zuwa N905 kowace lita.

Sabon farashin, ya nuna cewa an rage Naira 15 ga kowace lita, kamar yadda aka wallafa a dandalin sada zumunta na matatar Dangote a ranar Alhamis.

Haka farashin yake a hannun manyan dillalan mai tare da haɗin gwiwar matatar, ciki har da MRS, Ardova, Heyden, Optima Energy, Techno Oil, da Hyde Energy.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata