DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu ne dan takara daya tilo na jam’iyyarmu a zaben 2027 – Gwamnonin APC

-

Gwamnonin jam’iyyar APC sun amince da Shugaba Bola Tinubu a matsayin dan takara daya tilo na jam’iyyar a zaben 2027.

Gwamnan Jihar Imo kuma shugaban dandalin gwamnonin APC, Hope Uzodima ne ya bayyana haka a babban taron jam’iyyar da ya gudana a fadar Shugaban Kasa.

Google search engine

Uzodinma ne ya fara ayyana wannan kudiri yayin da gwamnan Kaduna, Uba sani ya mara masa baya inda daga bisani kuma sauran gwamnonin suka amince da Tinubu a matsayin dan takara tilo a jam’iyyar.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Cristiano Ronaldo zai yi ritaya daga kwallon kafa nan ba da jimawa ba

Shahararren ɗan wasan ƙwallon ƙafa na ƙasar Portugal, Cristiano Ronaldo, ya bayyana cewa zai yi ritaya daga wasa nan ba da jimawa ba, yana mai...

Gwamnatin Nijeriya ta mayar ma Amurka da martani kan kalamanta ga kasar

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa gwamnatin Amurka ta yi kuskuren fahimtar hakikanin matsalolin tsaro a kasar. Ministan yada labaran Nijeriya, Mohammed Idris, ya ce gwamnatin Nijeriya...

Mafi Shahara