DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotu ta yanke wa Murja Kunya hukuncin zaman gidan yari ko biyan tara kan cin zarafin Naira

-

Babbar kotun Tarayya da ke Kano ƙarƙashin Mai shari’a Simon Amobeda ta yanke wa Murja Ibrahim Kunya hukuncin watanni shida a gidan gyaran hali ko biyan tarar Naira 50,000, bayan ta amsa laifin cin zarafin Naira.

EFCC ce ta gurfanar da Murja a watan Janairun 2025 bisa karya dokar CBN da ta haramta cin zarafin Naira. An bayar da belinta, amma ta ki bayyana a kotu har sai da aka sake kama ta a ranar 16 ga Maris 2025.

Google search engine

An sake gurfanar da ita a ranar 20 ga Mayu, inda ta amsa laifinta, a hukuncin, kotu ta umurce ta zama jakadiyar EFCC da CBN don wayar da kai kan illar cin zarafin Naira ta hanyar shafinta na sada zumunta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara