Majalisar Dattawa ta amince da kasafin kuɗi na Naira tiriliyan 1.8 na shekarar 2025 ga Hukumar Gudanarwar Birnin Tarayya (FCTA). Wannan ya biyo bayan gabatar da rahoton Kwamitin FCT a zauren majalisa daga Shugaban Kwamitin, Sanata Bomai Ibrahim daga jihar Yobe ya gabatar.
Jaridar Daily Nigerian ta ruwato cewa, kasafin ya ƙunshi Naira biliyan 106 don albashin ma’aikata, Naira biliyan 352 don kudaden gudanarwa, wanda ya kai jimillar kashe kuɗin yau da kullum Naira biliyan 502.
An kuma ware Naira tiriliyan 1.3 don manyan ayyuka, inda kashi 85% daga ciki zai tafi kan ayyukan da ake gudanarwa, yayin da kashi 50% zai je sabbin ayyuka.
Sanata Bomai ya bayyana cewa an tattauna kasafin ne tare da Ministan Abuja da wasu muhimman jami’an FCTA kafin gabatar da shi.



