DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tilas aka min na amince ni na kafa gidan rediyon Biyafara -Nnamdi Kanu

-

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta amince da bidiyo uku, ciki har da wanda ke nuna shugaban haramtacciyar ƙungiyar IPOB, Nnamdi Kanu, na duba na’urar Radio Biafra da aka ce an shigo da ita ƙasar ta ɓoye.

A ci gaba da shari’ar zargin ta’addanci, Kanu ya ce ya furta wasu kalamai ne cikin tsoro a 2015, sai dai shaida daga DSS ya ce ba a tilasta masa ba, kuma ya karyata zargin barazana daga jami’an DSS.

Google search engine

An kuma shigar da bayanan da Kanu ya rubuta a DSS da bidiyon hirarsa da Sahara Reporters, inda ya kira Najeriya da “Zoo”.

Mai shari’a James Omotosho cikin rahoton da gidan talabijin na Channels ya wallafa ya ce kotun za ta bi diddigin ikrarin da yayi don tantance sahihancin bayanan da DSS ta gabatar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara