Gwamnan Jihar Kogi, Ahmed Ododo, ya taya Shugaba Bola Tinubu murnar cika shekara biyu a mulki, yana mai yabawa da jagorancinsa na hangen nesa da sauye-sauyen da ke kara sanya juriya a tsakanin ‘yan kasa.
A wata sanarwa daga mai ba shi shawara kan harkokin yada labarai, Ismail Isah, Ododo ya ce Najeriya ta fara cin gajiyar sauye-sauyen tattalin arzikin da aka fara tun shekarar farko.



