DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnan Kano Abba Kabir ya umurci da a binciki musabbabin rage albashin wasu ma’aikatan jihar, har ma ya kafa kwamiti

-

 

Abba Kabir Yusuf

Google search engine

Gwamna Abba Kabir Yusuf na Kano ya kaddamar da kwamitin da zai bincike matsalolin rashin biyan albashi da ya shafi wasu ma’aikatan gwamnati a jihar.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar a ranar Alhamis ya bayyana matakin a matsayin cin zarafin ma’aikata da ba za a amince da shi ba da kuma cin amanar al’umma,gwamnan ya sha alwashin fallasa tare da hukunta wadanda suke da hannu wajen aikata hakan.

Ya ce gwamnati ba za ta amince da duk wani zalunci da ake yi wa ma’aikatan ta ba, duk wanda aka samu da hannu a cikin wannan rashin imani tabbas, zai fuskanci fushin doka.

An umurci kwamitin da ya gudanar da cikakken bincike kan albashin jihar daga Oktoba 2024 zuwa Fabrairu 2025, gano ma’aikatan da abin ya shafa, tantance su, tare da ba da shawarar gyara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Manyan Jami’an soji za su fuskanci ritayar dole bayan sauye-sauye a fannin tsaron Nijeriya

Rahotanni sun tabbatar da cewa akwai manyan jami'an sojin Nijeriya  masu mukamin Janar akalla 60 da za su fuskanci ritayar dole, biyo bayan sauye-sauyen da...

Rashin gogewar siyasa ta sa ban tsayar da El-Rufa’i don ya gaje ni ba – Obasanjo

Tsohon shugaban Nijeriya Olusegun Obasanjo ya bayyana cewa ya ki tsayar da tsohon gwamnan jihar Kaduna Malam Nasiru Elrufa'i don ya gaje a shekarar 2007...

Mafi Shahara