Tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya bayyana alhininsa kan mutuwar sama da mutum 100 a ambaliya da ta faru a Jihar Neja da kuma hadarin mota da ya yi sanadin mutuwar matasa 22 ‘yan wasa da jagororinsu a Jihar Kano.
Cikin sanarwar da ya wallafa a shafinsa na Facebook wanda mai magana da yawunsa Malam Garba Shehu ya fitar, Buhari ya ce lamarin ya girgiza shi matuƙa, yana mai mika ta’aziyya ga iyalai da gwamnatocin jihohin biyu. Ya roki Allah ya jikansu, ya kuma ba waɗanda suka jikkata sauƙi.



