DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Nijeriya ta musanta zargin babban jami’in Binance cewa ‘yan majalisa 3 sun nemi cin hancin $150m

-

Gwamnatin Nijeriya ta musanta zargin babban jami’in kamfanin Binance Tigran Gambaryan wanda ya shafe watanni takwas yana tsare a hannun hukumomin Nijeriya bisa zargin rashawa.
Gambaryan wanda dan kasar Amurka ne, an sake shi bayan da gwamnatin kasar ta shiga tsakani, sai dai a wani sako da ya wallafa a shafinsa na X ya zargi gwamnatin Nijeriya da tsare shi ba bisa ka’ida ba.
Ya kuma yi zargin cewa wasu ‘yan majalisa uku sun nemi ya basu cin hanci na dala miliyan 150.
A martanin gwamnatin, ta hannun ministan yada labarai Mohammed Idris, ta ayyana kalaman a matsayin yunkurin yada labaran karya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar dokokin Nijeriya ta kayyade adadin kudin za a kashe wajen kamfe

Majalisar dokokin Nijeriya ta kayyade Naira biliyan 10 ga masu takarar shugaban kasa da Naira biliyan 3 ga masu takarar Gwamna a matsayin adadin kudin...

Sojojin Nijeriya sun dakile harin ‘yan bindiga a jihar Borno

Rundunar sojin Nijeriya karkashin shirin 'Operation Hadin Kai' ta samu nasarar dakile wani hari da 'yan ta'adda suka shirya kaddamarwa a yankin Bitta daga tsaunukan...

Mafi Shahara