DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An shiga wata na biyu a gyaran matatar mai ta Fatakwal

-

Matatar mai ta Port Harcourt da ke karkashin kamfanin man Nijeriya NNPCL ta kwashe fiye da wata guda a rufe saboda gyara, ba ta dawo aiki ba.

Wannan na zuwa ne bayan da Tsohon jami’in hulda da jama’a na NNPC, Olufemi Soneye, ya bayyana a watan Mayu cewa za a rufe matatar don gyare-gyare.

Google search engine

Rahotanni sun ce hukumar EFCC na binciken kudaden da aka ware don gyaran matatun mai uku a Nijeriya da suka hada da: dala biliyan $1.5 don matatar mai ta Port Harcourt, da dala miliyan $740m don matatar man Kaduna, da kuma dalar Amurka miliyan $657m don Warri.

Yanzu haka dai tsoffin shugabannin matatun, ciki har da Umar Isa (Tsohon CFO na NNPC), suna fuskantar bincike kan zargin almundahana da karkatar da kudi kamar yadda jaridar Punch ta gano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara