DCL Hausa Radio
Kaitsaye

PDP ta maido wa Samuel Anyanwu mukaminsa na sakataren jam’iyyar na kasa

-

PDP ta maido wa Samuel Anyanwu mukaminsa na sakataren jam’iyyar na kasa

Jam’iyyar PDP ta dawo da Samuel Anyanwu a matsayin sakataren jam’iyya na kasa bayan ganawarta da hukumar INEC a ranar Talata.

Google search engine

Shugaban rikon kwarya na PDP, Umar Damagum, ya bayyana hakan a taron manema labarai a Abuja, inda ya ce Anyanwu zai ci gaba da aiki a matsayin sakataren kamar yadda gidan Talabijin na Channels ya tabbatar.

Jam’iyyar ta kuma soke taron NEC da aka shirya gudanarwa a ranar 30 ga Yuni, inda ta maye gurbinsa da taron masu ruwa da tsaki na jam’iyyar.

A baya hukumar zaben Nijeriya INEC ta ce ba za ta halarci taron NEC na PDP ba saboda rikicin shugabancin sakataren jam’iyyar da kuma sabanin da ke cikin sa hannun takardun da aka aikewa hukumar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara