DCL Hausa Radio
Kaitsaye

INEC na duba buƙatun kungiyoyi 110 da ke neman rigista a matsayin jam’iyyun siyasa a Najeriya

-

Hukumar zabe ta kasa INEC ta bayyana cewa ta karɓi wasikun buƙatun rajistar sabbin jam’iyyu 110 daga kungiyoyi daban-daban har zuwa Litinin, 23 ga watan Yunin, 2025.

Shugaban hukumar, Farfesa Mahmood Yakubu, ya ce ana ci gaba da duba buƙatun bisa doka da tsarin da aka shimfiɗa inda ya ce sun riga sun amsa duk buƙatun da aka aika, banda guda shida da za a amsa kafin ƙarshen mako.

Google search engine

Hukumar ta INEC ta fitar da cikakken bayanan jerin sunayen kungiyoyin da ke neman rajista da sunayensu, takaitattun haruffansu, adireshisu, da shugabanninsu a jumlace.

Kuma hukumar cikin sakon da ta wallafa a shafinta na Facebook ta ce za a wallafa jerin gwanon su a shafin yanar gizo da kafafen sada zumunta na hukumar don samun gamsashshiyar fahimta kan kudirin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara