Majalisar Wakilai ta yi kira ga gwamnatin tarayya da ta gaggauta kafa sansanin sojojin Nijeriya a garin Yelwata dake kan iyaka a karamar hukumar Guma ta jihar Benue, biyo bayan halaka mutane da ake zargin wasu mahara dauke da makamai suka yi wa sama da mutane 200 a ranar 14 ga watan Yuni.
Wannan kudiri dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Makurdi/Guma,a majalissar Dickson Tarkighir ya gabatar.
Dan majalisar ya kuma yi tir da mummunan harin, yana mai nuni da cewa kisan kiyashin na Yelwata ya kara dagula harkokin jinkai a yankin.