DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Kaduna ta yi watsi da ikiranin da El-Rufai ya yi kan ayyukan da Tinubu ya kaddamar cewa shi ne ya fara su

-

Gwamnatin jihar Kaduna ta yi watsi da ikirarin da wani tsohon gwamnan jihar, Nasir El-Rufai ya yi na cewa dukkanin ayyukan da shugaban kasa Bola Tinubu ya kaddamar a jihar kwanan nan an fara su ne a gwamnatinsa.

El-Rufai, wanda ya mulki Kaduna daga 2015 zuwa 2023, a wata hira da manema labarai a ranar Litinin ya bayyana cewa ayyukan da shugaba Tinubu ya kaddamar a ranar Alhamis din da ta gabata, aikinsa ne

Google search engine

Sai dai kuma a wani martani da ya mayar, babban sakataren yada labarai na gwamna Uba Sani, Ibraheem Musa ya bayyana ikirarin tsohon gwamnan a matsayin karya ce tsantsa da kuma yunkurin canza tunanin mutane.

A wata sanarwa da ya fitar ranar Talata, ya bayyana cewa ayyukan da ake magana a kai an fara su ne kuma an kammala su a karkashin gwamnati mai ci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara