DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Rundunar sojin saman Nijeriya sun yi ajalin ‘yan bindiga da dama a jihar Neja

-

Sojojin saman Nijeriya dake karkashin rundunar Operation Fansar yamma, sun yi luguden wuta ga ‘yan bindiga da suka kai hare-hare na baya-bayan nan a jihar Neja, tare da tallafi ta kasa daga sojojin kasar.

Harin wanda aka aiwatar tsakanin 24 zuwa 26 ga watan Yuni, 2025, an gudanar da su ne bisa ingantattun bayanan sirri, a cewar sanarwar da daraktan yada labarai na rundunar, Air Commodore Ehimen Ejodame, ya fitar ranar Juma’a a Abuja.

Google search engine

Ya ce rundunar, hadin gwiwa sauran hukumomin tsaro, sun gano ‘yan ta’adda masu kai hare-hare da satar shanu a yankunan Kakihun da Kumbashi.

Cikin hanzari rundunar ta tura da jirage domin kai hare-hare wanda aka yi nasara tare da lalata musu kayayyaki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara