Tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo ya caccaki gwamnatocin Nijeriya da sauran kasashen Afirka kan yadda suke dogaro da tallafin kasashen waje, da rashin shugabanci nagari, da gazawar tsarin dimokradiyya.
Obasanjo ya bayyana haka ne lokacin da yake jawabi a wajen taron shekara-shekara na Afreximbank karo na 32 a Abuja a ranar Juma’a, inda ya ce kasashen Afirka sun kasa samun ci gaba da rashin inganci a tsarin mulki da kuma gudanar da mulki yadda ya dace.
A cewarsa, kasashe kamar Nijeriya, Masar, Habasha, Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo, da Afirka ta Kudu, ya kamata su jagoranci ayyukan ci gaban nahiyar idan aka yi la’akari da yawan al’umma, albarkatunsu,da karfin tattalin arzikinsu.
Ya ce a maimakon haka, wadannan kasashe sun ci gaba da samun koma baya saboda rashin kyayyawan jagoranci.
Obasanjo ya bayyana cewa idan anason ci gaban Afrika sai dai idan wadannan manyan kasashen sun fara nuna ci gaba mai ma’ana da kyakkyawan jagoranci.