DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Yawan dogaro da kasashen waje ke hana Nijeriya samun ci gaba

-

Tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo ya caccaki gwamnatocin Nijeriya da sauran kasashen Afirka kan yadda suke dogaro da tallafin kasashen waje, da rashin shugabanci nagari, da gazawar tsarin dimokradiyya.

Obasanjo ya bayyana haka ne lokacin da yake jawabi a wajen taron shekara-shekara na Afreximbank karo na 32 a Abuja a ranar Juma’a, inda ya ce kasashen Afirka sun kasa samun ci gaba da rashin inganci a tsarin mulki da kuma gudanar da mulki yadda ya dace.

Google search engine

A cewarsa, kasashe kamar Nijeriya, Masar, Habasha, Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo, da Afirka ta Kudu, ya kamata su jagoranci ayyukan ci gaban nahiyar idan aka yi la’akari da yawan al’umma, albarkatunsu,da karfin tattalin arzikinsu.

Ya ce a maimakon haka, wadannan kasashe sun ci gaba da samun koma baya saboda rashin kyayyawan jagoranci.

Obasanjo ya bayyana cewa idan anason ci gaban Afrika sai dai idan wadannan manyan kasashen sun fara nuna ci gaba mai ma’ana da kyakkyawan jagoranci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tarihin marigayi Aminu Dantata

Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un. Najeriya ta yi babban rashi – na dattijo, attajiri, mai hangen nesa da zuciya mai tausayi: Alhaji Aminu Alhassan...

Bayan shafe watanni 23, Ganduje ya ajiye mukamin shugabancin APC

Ta dai tabbata, Abdullahi Umar Ganduje ya yi murabus daga shugabancin jam'iyyar APC ta kasa. Tsohon Gwamnan jihar Kanon ya ajiye mukamin nasa da yammacin Juma'ar...

Mafi Shahara