Shugaban majalisar Malamai ta kasa reshen jihar Kano Sheikh Ibrahim Khalil ya ce za su yi wa marigayi Aminu Alhassan Dantata, Salatul Ga’ib wato jana’izar da ake yi wa mutumin da babu gawarsa a kusa.
Sheikh Khalil ya sanar da haka a shafinsa na Facebook, yana mai cewa matakin hakan ya biyo bayan sanarwar mutuwar attajirin da aka yi a wannan Asabar daga kasar Hadaddiyar Daular Larabawa.
Malam Khalil ya ce za a yi jana’izar karfe 2pm a masallacin masallacin Umar Bin Kattab da ke Dangi a cikin birnin Kano.