DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jaridar Punch ta gano hakikanin abin da ya sa Ganduje ya ajiye mukamin shugabancin APC

-

Bayanai sun fara fita dalla-dalla kan dalilan da suka sa shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Abdullahi Ganduje, ya yi murabus daga mukaminsa a ranar Juma’a.

Rahoton da jaridar PUNCH ta samu daga majiya mai ƙarfi ya nuna cewa Ganduje ya ajiye mukaminsa ne saboda rahotannin cewa tsohon gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, na shirin shiga jam’iyyar APC.

Google search engine

Tun da misalin ƙarfe 3 na rana a ranar Juma’a, wasu da ke aiki a sakatariyar jam’iyyar ta ƙasa sun shaida wa jaridar cewa tsohon shugaban jam’iyyar ya fara barazanar yin murabus saboda yarjejeniyar da aka ce ta faru tsakanin Shugaba Bola Tinubu da Kwankwaso don shigar Kwankwaso jam’iyyar.

Wata majiya ta bayyana cewa duk manyan jami’an jam’iyyar, ciki ha da sakataren jam’iyya na ƙasa, Ajibola Basiru, sun yi ƙoƙarin hana Ganduje ajiye mukaminsa.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara