DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jaridar Punch ta gano hakikanin abin da ya sa Ganduje ya ajiye mukamin shugabancin APC

-

Bayanai sun fara fita dalla-dalla kan dalilan da suka sa shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Abdullahi Ganduje, ya yi murabus daga mukaminsa a ranar Juma’a.

Rahoton da jaridar PUNCH ta samu daga majiya mai ƙarfi ya nuna cewa Ganduje ya ajiye mukaminsa ne saboda rahotannin cewa tsohon gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, na shirin shiga jam’iyyar APC.

Google search engine

Tun da misalin ƙarfe 3 na rana a ranar Juma’a, wasu da ke aiki a sakatariyar jam’iyyar ta ƙasa sun shaida wa jaridar cewa tsohon shugaban jam’iyyar ya fara barazanar yin murabus saboda yarjejeniyar da aka ce ta faru tsakanin Shugaba Bola Tinubu da Kwankwaso don shigar Kwankwaso jam’iyyar.

Wata majiya ta bayyana cewa duk manyan jami’an jam’iyyar, ciki ha da sakataren jam’iyya na ƙasa, Ajibola Basiru, sun yi ƙoƙarin hana Ganduje ajiye mukaminsa.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnan Bauchi ya sanya hannu kan dokar kirkirar sabbin masarautu 13 a fadin jihar

Gwamnan Bauchi Bala Muhammad ya sanya hannu kan dokar kirkirar sabbin masarautu 13 a fadin jihar. Daily Trust ta ruwaito cewa a lokacin da yake sanya...

Kenya da Senegal sun kulla yarjejeniyar shige da fice ba tare da biza ba

Gwamnatocin Kenya da Senegal sun bai wa juna damar shige da fice ga 'yan kasashensu ba tare da biza ba na tsawon kwanaki 90. DW Africa...

Mafi Shahara