DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hukumar zaben Nijeriya INEC ta karɓi ƙarin takardu 12 da ke neman rijistar sabbin jam’iyyu

-

Hukumar zaben Nijeriya INEC ta bayyana cewa ta karɓi ƙarin buƙatun rajista guda 12 daga ƙungiyoyin da ke neman zama jam’iyyun siyasa a kasar, inda hakan ya kai yawan waɗanda ke neman rajistar zuwa 122.

INEC ta bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da Kwamishinan Ƙasa mai kula da Yada Labarai da Ilimin Zaɓe, Mista Sam Olumekun, ya fitar a ranar Alhamis.

Google search engine

Sanarwar ta jaddada cewa ana aiwatar da tantance waɗannan buƙatu cikin gaskiya da adalci, kuma hukumar za ta rika sanar da ‘yan ƙasa ci gaban da ake samu.

Jaridar The Nation ta ce hukumar ta kuma ja hankalin ƙungiyoyin da ke neman rajista da su kasance da daidaito wajen bayyana shugabanninsu don guje wa tsaiko a cikin aikin tantancewa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara