Tsohon gwamnan jihar Nasarawa kuma jigo a jam’iyyar APC, Sanata Tanko Al-Makura, ya bayyana cewa a shirye yake ya yi aiki a duk irin matsayin da Shugaba Bola Tinubu ya nada shi, muddin hakan zai kawo cigaba ga jam’iyya da kasa.
A wata hira da ya yi da Trust TV, Al-Makura ya ce, “Idan Shugaban kasa ya ce min, ‘Al-Makura ina so ka dinga share teburina duk Litinin,’ zan je, in share, in tafi cikin farin ciki da gamsuwa.”
Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ake ta kiraye-kirayen daga ‘yan bangaren CPC da yankin Arewa ta Tsakiya da a nada Al-Makura a matsayin sabon shugaban jam’iyyar APC na kasa, bayan murabus din Dr Abdullahi Umar Ganduje.



