DCL Hausa Radio
Kaitsaye

A shirye nake na yi aiki a kowane matsayi da Shugaba Tinubu zai bani – Tanko Almakura

-

Tsohon gwamnan jihar Nasarawa kuma jigo a jam’iyyar APC, Sanata Tanko Al-Makura, ya bayyana cewa a shirye yake ya yi aiki a duk irin matsayin da Shugaba Bola Tinubu ya nada shi, muddin hakan zai kawo cigaba ga jam’iyya da kasa.

A wata hira da ya yi da Trust TV, Al-Makura ya ce, “Idan Shugaban kasa ya ce min, ‘Al-Makura ina so ka dinga share teburina duk Litinin,’ zan je, in share, in tafi cikin farin ciki da gamsuwa.”

Google search engine

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ake ta kiraye-kirayen daga ‘yan bangaren CPC da yankin Arewa ta Tsakiya da a nada Al-Makura a matsayin sabon shugaban jam’iyyar APC na kasa, bayan murabus din Dr Abdullahi Umar Ganduje.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara