DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hadiman gwamnan Kano yanzu sun zarta 300, bayan sanar da sabbin nade-nade 19 – Daily Trust

-

Gwamnan Jihar Kano Abba Kabir Yusuf, ya amince da naɗin karin manyan mataimaka na musamman guda 19, domin ƙarfafa harkokin mulki da inganta ayyukan gwamnati.

Mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a.

Google search engine

Rahoton jaridar Daily Trust ya bayyana cewa Gwamna Abba Kabir na da kusan mataimaka 290 kafin wadannan mukamai, waɗanda suka haɗa da Masu Ba da Shawara na Musamman, Manyan Mataimaka na Musamman da kuma Masu Ba da Rahoto na Musamman.

Gwamnatin jihar ta Kano ta bayyana ƙwarin guiwa cewa sabbin waɗanda aka naɗa za su yi amfani da ƙwarewarsu da jajircewarsu wajen taimakawa tafiyar da mulki bisa hangen nesa a jihar.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara