Monday, April 6, 2026
HomeSiyasaTsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar na mazabarsa ta Banshika a karamar hukumar Hong, jihar Adamawa.

A wasikar da aka sanya ranar 29 ga Yuni, 2025, Babachir ya ce ficewarsa ta fara aiki nan take, tare da bayyana cewa zai bayyana sabuwar jam’iyyar da zai shiga a nan gaba kadan.

Ya ce matakin na daya daga cikin shirinsa na hada kai da sauran ‘yan Najeriya domin gyara kasar daga kuskure da gazawar tsohuwar jam’iyyarsa ta APC kamar yadda jaridar Daily Nigerian ta ambato.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata