DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin tarayya ta bai wa iyalan wanda ya zana tutar Nijeriya tallafin milyan 30

-

 

Shugaba Tinubu

Google search engine

Gwamnatin tarayya ta bayar da gudummawar N30m ga iyalan wanda ya yi zanen tutar Nijeriya, Taiwo Akinkunmi, a ranar Alhamis.

Babban daraktan hukumar wayar da kan jama’a ta kasa Lanre Issa Onilu tare da rakiyar daraktan hukumar na jihar Oyo Olukemi Afolayan ne suka gabatar da cakin kudin a madadin gwamnatin tarayya a fadar gwamnati da ke Elebu, Ibadan, jihar Oyo.

Jaridar PUNCH ta ruwaito cewa Marigayi Akinkunmi ya rasu ne a ranar 29 ga watan Agustan 2023, yana da shekaru 87 a duniya.

A ranar 4 ga Satumba, 2023, Shugaba Bola Tinubu ya aike da wata tawaga karkashin jagorancin ministan yada labarai da wayar da kan jama’a Mohammed Idris, domin yi wa iyalan ta’aziyya, inda gwamnatin ta yi alkawarin tallafa wa iyalan marigayin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara