Tsohon gwamnan jihar Kogi, Alhaji Yahaya Bello, ya auri mata cikon ta huɗu mai suna Hiqma, a wani bikin sirri da aka gudanar a karshen mako a birnin Abuja.
Bikin auren, wanda aka shirya cikin ruwan sanyi, ya samu halartar ‘yan Uwa da abokin arziki na kusa da tsohon gwamnan.
Matar sa ta uku, Hafiza Yahaya Bello ce, ta tabbatar da sabon auren a sakon da ta wallafa a shafinta na Instagram, inda ta bayyana gamsuwa da shigowar sabuwar amaryar tare da yi mata maraba da fatan alheri.
Yahaya Bello, wanda ya mulki Jihar Kogi daga shekarar 2016 zuwa 2023 karkashin jam’iyyar APC, ya kulle kofar aure, da matansa hudu Amina Oyiza Bello, Rashida Yahaya Bello, Hafiza Yahaya Bello sai sabuwar amaryar, Hiqma.



