DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ficewar Atiku daga PDP ya saba faruwa, muna sa ran zai dawo – Damagum

-

Shugaban riko na jam’iyyar PDP Ambasada Iliya Damagum, ya bayyana ficewar tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, daga jam’iyyar a matsayin wani lamari da ba sabon abu ba.

Da yake zantawa da manema labarai a Bauchi ranar Juma’a, Damagum ya ce jam’iyyar PDP ba ta ji wani mamaki ko damuwa ba dangane da ficewar Atiku, domin ya saba da irin wannan a shekarun baya.

Google search engine

“Yana cikin tsarin da muka saba da shi — ya tafi, ya dawo. Wannan wani salo ne na siyasarsa, ba mu ɗauke shi a matsayin rabuwa ta dindindin ba,” in ji Damagum.

Wannan na zuwa ne yayin da rahotanni ke cewa Atiku na ƙoƙarin shiga jam’iyyar hadaka ta ADC a hukumance, a shirin tunkarar zaɓe mai zuwa.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara