Tsohon Gwamnan Jihar Benue, Samuel Ortom, ya bayyana cewa bai taba nadamar kin yiwa tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar aiki a zaben 2023 ba, duk da cewa a lokacin suna jam’iyya daya.
Ortom ya bayyana hakan ne yayin wata hira da gidan talabijin na Channels, inda ya ce siyasa ba wai yin biyayya ga mutum ko jam’iyya ba ne, amma tsayawa kan muradun jama’a da nuna gaskiya.
Tsohon gwamnan, wanda ya kasance cikin kungiyar G5, ta gwamnoni biyar da suka bijirewa Atiku a zaben shugaban kasa na 2023, ya kuma bayyana cewa sabuwar hadakar siyasa da Atiku ke jagoranta ba zata kai ko’ina ba, yana mai cewa “mutane sun gane gaskiya kuma sun gaji da siyasar son rai.


