Majalisar dattawan Nijeriya ta bayyana shirinta na gudanar da zama na musamman a ranar Laraba mai zuwa domin nuna girmamawa da tunawa da marigayi tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari.
Wannan zama na musamman zai mayar da hankali ne kan gagarumar gudunmawar da marigayin ya bayar wajen ci gaban Nijeriya, tun daga lokacin da ya hau mulki har zuwa saukarsa, kamar yadda gidan talabijin na Channels TV ya ruwaito.
A makon da ya gabata, Majalisar Zartaswa ta Tarayya ma ta gudanar da irin wannan zama domin tunawa da rayuwa da hidimar marigayin, wanda ya rasu kwanan nan.
Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, a yayin taron Majalisar Zartaswa, ya bayyana Buhari a matsayin shugaba wanda ya jagoranci kasar cikin gaskiya da rikon amana, yana mai cewa Buhari ya bar tarihi mai kyau da za a ci gaba da tunawa da shi a tarihin Nijeriya.



