Monday, April 6, 2026
HomeSiyasaBabu kanshin gaskiya a labarin cewa Gwamna Mai Mala zai bar APC...

Babu kanshin gaskiya a labarin cewa Gwamna Mai Mala zai bar APC ya koma ADC – Gwamnatin jihar Yobe

Gwamnatin Jihar Yobe ta musanta rahotannin da ke cewa Gwamna Mai Mala Buni na shirin sauya sheka zuwa jam’iyyar ADC.

Daraktan Yada Labarai da Harkokin Jama’a na Gwamnan, Mamman Mohammed, ne ya bayyana hakan a wata ganawa da manema labarai a Damaturu, babban birnin jihar.

Mohammed ya ce an riga an musanta wannan rahoto tun da farko, don haka bai kamata a dauke shi da muhimmanci ba.

A cewarsa, batun cewa Buni zai koma jam’iyyar ADC ba gaskiya ba ne, rahoton kuma bai da tushe balle makama.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata