DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tinubu ya ja kunnen gwamnoni kan a rika ganin tasirin kudaden da gwamnatinsa ke basu a kasa

-

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya bukaci gwamnonin jihohi, musamman na jam’iyyar APC, da su tabbatar da cewa makudan kuɗaɗen da aka raba musu ta hannun FAAC sun haifar da gamsassun ayyukan ci gaba, musamman a matakin ƙananan hukumomi.

Shugaban ya bayyana haka ne yayin taron Kwamitin Zartaswa na Ƙasa (NEC) na jam’iyyar APC, inda ya jaddada cewa duk da rabar da Naira tiriliyan 11.195 ga jihohi da ƙananan hukumomi daga watan Yuni 2024 zuwa Yuni 2025, har yanzu mutane da dama na ƙara korafi kan rashin ayyukan ci gaba a matakin ƙasa.

Google search engine

Gidan talabijin na Channels ya ce binciken FAAC ya nuna cewa cikin Naira tiriliyan 27 da aka raba tsakanin Janairu zuwa Yuni 2025, gwamnatin tarayya ta samu Naira tiriliyan 6.034, jihohi sun samu Naira tiriliyan 6.492, yayin da ƙananan hukumomi suka karɓi Naira tiriliyan 4.704.

Har wa yau, gwamnatin tarayya ta bayyana cewa ta tara Naira tiriliyan 14.27 a matsayin haraji cikin watanni shida na farkon shekarar 2025, karin 43% idan aka kwatanta da kudin haraji da aka tara a rabin farkon shekarar 2024.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara