DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan bindiga 45 sun sheka lahira a hannun dakarun hadin gwiwar sojin Nijeriya a jihar Neja

-

Dakarun sojin Najeriya tare da hadin gwiwar jami’an DSS da wasu ‘yan sa-kai, sun yi ajalin ‘yan bindiga 45 da suka kai hari garin Iburu a karamar hukumar Shiroro, Jihar Neja da yammacin Juma’a.

Bayanan sirri daga DSS sun gano cewa ‘yan ta’addan na tafe da babura da dama domin kai hari a yankin, lamarin da ya sa aka sanar da sojoji da ke shirin dakile barazanar.

Google search engine

Bayan sauran bayanai daga mazauna yankin, an ce sun kirga akalla gawarwaki 40 na ‘yan bindigar da kuma babura da dama da aka kone a fafatawar.

A yayin artabun, ‘yan sa-kai biyu sun rasa rayukansu, yayin da hudu ke jinya a babban asibitin jiya na jihar sakamakon harbin bindiga kamar yadda rahoton jaridar The Nation ya tabbatar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara