Dakarun sojin Najeriya tare da hadin gwiwar jami’an DSS da wasu ‘yan sa-kai, sun yi ajalin ‘yan bindiga 45 da suka kai hari garin Iburu a karamar hukumar Shiroro, Jihar Neja da yammacin Juma’a.
Bayanan sirri daga DSS sun gano cewa ‘yan ta’addan na tafe da babura da dama domin kai hari a yankin, lamarin da ya sa aka sanar da sojoji da ke shirin dakile barazanar.
Bayan sauran bayanai daga mazauna yankin, an ce sun kirga akalla gawarwaki 40 na ‘yan bindigar da kuma babura da dama da aka kone a fafatawar.
A yayin artabun, ‘yan sa-kai biyu sun rasa rayukansu, yayin da hudu ke jinya a babban asibitin jiya na jihar sakamakon harbin bindiga kamar yadda rahoton jaridar The Nation ya tabbatar.



