DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Dan takarar mataimakin gwamnan Kaduna a zaben 2023 ya fice daga jam’iyyar PDP zuwa ADC

-

John Ayuba, wanda ya tsaya takarar mataimakin gwamnan Jihar Kaduna a ƙarƙashin jam’iyyar PDP a zaben 2023, ya fice daga jam’iyyar tare da komawa jam’iyyar ADC.

Rahoton jaridar Punch ya Ambato wasikar da Ayuba ya tabbatar da sauya shekar tasa ne, da ya aike wa shugaban jam’iyyar PDP na unguwar Ungwan Gaiya, da ke karamar hukumar Zangon Kataf.
Ya bayyana rashin jagoranci da cin amanar jam’iyya daga manyan jiga-jigai na ƙasa a matsayin dalilin ficewarsa.

Google search engine

Sa’annan ya kuma zargi wasu jiga-jigan PDP da cin amanar ɗan takarar shugaban ƙasa a zaben da ya gabata da kuma gaza ɗaukar matakin gyara tafiyar har zuwa yanzu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara