Shahararren ɗan kasuwa a Afirka Aliko Dangote ya yaba wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa manufofinsa da ke haifar da daidaito a kasuwar canjin kudi da kuma karfafa Naira.
Dangote ya bayyana hakan ne lokacin da ministar masana’antu, kasuwanci da zuba jari, Dr Jumoke Oduwole, ta kai ziyara zuwa masana’antarsa ta Dangote Refinery da Fertiliser da ke Ibeju-Lekki, Legas.
Ya ce sabon tsarin “Naira-for-Crude” da dokar “Nigeria First” sun taimaka matuka wajen magance matsalar samar da danyen mai ga matatun cikin gida.
Dangote ya jaddada cewa sayen danyen mai da Naira zai taimaka wajen cika bukatun kasuwa da kuma bunkasa tattalin arzikin kasa.
Ya bayyana cewa karancin sauye-sauye a canjin Naira da Dala ya dawo da kwarin gwiwa ga masu zuba jari, kuma yana fatan Naira za ta kara karfi nan gaba kamar yadda jaridar Daily Tust ta ambato.



