DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Wafaa Saeed Abdelatef ta zama babbar jami’ar asusun UNICEF a Nijeriya

-

Asusun kula da kananan yara na majalisar dinkin duniya UNICEF ya sanar da Ms. Wafaa Saeed Abdelatef a matsayin wakiliyar asusuna Najeriya.

Kafin ta hau wannan mukami a Nijeriya, Ms Wafaa, ita ce wakiliyar asusun UNICEF a kasar Somalia.

Google search engine

Wafaa na da fiye da shekaru 20 tana yin hidima ga jama’a ta hanyar ayyukan Majalisar Dinkin Duniya. Ta yi aiki da OCHA, UNICEF da WFP a wurare masu fama da rikice-rikice da matsaloli masu tarin yawa, inda ta samu kwarewa wajen gudanar da shirye-shirye da hada kai tsakanin ayyukan jin kai da ci gaba. Ta yi ayyuka a kasashen sun hada da Sudan, Somalia, Indonesia, Pakistan, Syria da Ethiopia. Ta kuma rike manyan mukamai na shugabanci a OCHA, duka a New York da Geneva.

Kafin ta shiga tsarin Majalisar Dinkin Duniya a shekarar 2000, Wafaa ta yi aiki da kamfanoni masu zaman kansu, jami’o’i da kungiyoyin farar hula a kasar Sudan, inda ta mayar da hankali kan shirye-shiryen taimaka wa ‘yan gudun hijira da kuma kare muhalli.

Wafaa ta samu digiri na biyu (Master’s) a fannin zane-zanen gine-gine daga Jami’ar Katholieke Universiteit Leuven da ke kasar Belgium, digiri na biyu a fannin Tsarin Birane daga Jami’ar Khartoum, da kuma digiri na farko (Bachelor) a fannin zane-zanen gine-gine daga Jami’ar Khartoum, Sudan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara