DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ku jira sai zuwa 2031 tukuna – Shawarar George Akume kenan ga ‘yan siyasar Arewa da ke neman kujerar shugaban kasa

-

Sakataren Gwamnatin Tarayyar Nijeriya, Sanata George Akume, ya shawarci ‘yan siyasa daga yankin Arewa da su dakata har zuwa shekarar 2031 kafin su nemi kujerar shugaban kasa.

Akume ya bayyana haka ne a ranar Talata yayin wani taron tattaunawa na kwanaki biyu a Kaduna, wanda aka shirya domin karfafa hulɗa tsakanin gwamnati da ‘yan ƙasa.


Jaridar Punch ta ruwaito Akume na yabawa cibiyar Sir Ahmadu Bello bisa samar da dandalin tattaunawa domin inganta shugabanci da dimokuraɗiyya a ƙasar.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnan jihar Zamfara ya gabatar da kasafin kudi N861bn na 2026 ga majalisar dokokin jihar

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya gabatar da kasafin kuɗi na Naira biliyan 861 na shekarar 2026 a gaban majalisar dokokin Jihar a Gusau, yana...

Shugaba Tinubu ya aika da sunan Dambazau domin tantancewa a matsayin jaakada

Shugaba Bola Tinubu ya ya aike da tsohon ministan cikin gida, Abdulrahman Dambazau, wanda ya taba zama shugaban sojin ƙasa, a matsayin jakada domin tantancewa...

Mafi Shahara