DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tattalin arzikin Najeriya zai bunkasa daga 2025 zuwa 2026 – IMF

-

Asusun Lamuni na Duniya (IMF) ya sabunta hasashensa kan ci gaban tattalin arzikin Najeriya, inda ya ce zai kai kashi 3.4 cikin 100 a shekarar 2025 da 3.2% a 2026.

Wannan sabon rahoto na World Economic Outlook da aka fitar a watan Yuli 2025, ya fi hasashen da aka yi a watan Afrilu na 3.0% da 2.7%.

Google search engine

IMF ta kuma kara hasashen ci gaban tattalin arzikin duniya gaba É—aya zuwa 3.0% a 2025 da 3.1% a 2026, yayin da yankin Sub-Saharan Africa zai kai 4.0% a 2025 da 4.3% a 2026.

Sai dai, IMF ta shawarci kasashen yankin su dauki matakan gaggawa na gyaran tsarin mulki da hukumomi, duba da kalubalen tattalin arziki da suke fuskanta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara