DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamna Zulum na jihar Borno ya sallami wasu kwamishinoninsa biyu daga mukamansu

-

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya sauke kwamishinansa biyu daga muƙamansu.

Mai magana da yawun gwamnan, Dauda Iliya, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis.

Kwamishinonin da abin ya shafa su ne na Ma’aikatar Muhalli, Injiniya Emat Kois, da kuma Kwamishinan Hulɗa da Gwamnatoci da Harkokin Musamman, Honarabul Tukur Ibrahim.

Hakama gwamnan ya sanar da nadin Injiniya Mohammed Habib da Ibrahim Hala Hassan a matsayin sabbin kwamishinonin da za su maye gurbin waɗanda aka sauke.

Google search engine
Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara