DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shekara ɗaya da zanga-zangar matsin rayuwa a Nijeriya har yanzu ba ta sauya zani ba – Jagororin zanga-zangar

-

Watanni goma sha biyu bayan dubban ’yan Nijeriya sun fita kan tituna suna kokawa kan tsananin wahalar rayuwa da rashin shugabanci nagari, masu shirya zanga-zangar #EndBadGovernance da masana tattalin arziki sun ce halin da ake ciki ko dai bai canza ba, ko ma ya kara muni.

Zanga-zangar, wadda ta gudana daga ranar 1 zuwa 10 ga watan Agustan 2024, ta samo asali ne daga matsin tattalin arziki, hauhawar farashin kayan masarufi, karancin ayyukan yi da hauhawar farashin mai – lamarin da ya fusata ƴan kasar a sassa daban-daban.

Hakama kungiyar kare hakkin bil’adama ta Amnesty International ta bayyana cewa har yanzu gwamnati bata tabbatar da adalci ga wadanda aka kashe ko aka kama ba.

Rahoton Amnesty ya nuna cewa ’yan sanda sun kashe akalla mutane 24 a lokacin zanga-zangar tsakanin ranar 1 zuwa 10 ga Agusta a jihohin Kano, Katsina, Jigawa, Borno, Niger da Kaduna.

Google search engine

Wasu daga cikin masu zanga-zangar kuma an kama su tare da yi musu shari’a bisa tuhumar da ta bayyana da cewa karya ce.

Har ila yau, kungiyar ta Amnesty ta ce ana cigaba da gudanar da shari’u a wasu daga cikin jihohin da abin ya shafa ciki har da Abuja, ba tare da samun wani cikakken adalci ba ga wadanda suka rasa rayukansu ko aka ci zarafinsu.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara